Connect with us

Labarai

Gwamnatina ba za ta biya kuɗin fansa ko kuma yin sulhu ba- Shugaba Tinubu

Published

on

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ya ce, gwamnatinsa ba za ta biya kuɗin fansa ko yin sulhu da masu garkuwa da mutane ba, domin hakan na ƙara ƙarfafa ayyukan ta’addanci da ƴan bindiga.

 

Shugaba Tinubu ya bayyana haka ne yayin karɓar baƙuncin sarakunan gargajiya daga jihar Oyo a Abuja, inda ya ce gwamnatin tarayya ta ƙi amincewa da buƙatar masu garkuwa da ɗalibai da malamai 44 da aka sace a ƙaramar hukumar Oriire ta jihar Oyo, waɗanda suka nemi kuɗin fansa da kuma sakin wasu daga cikin abokan aikinsu da ke tsare.

 

Ya kuma bayyana cewa gwamnati na ƙarfafa tsarin tsaro tare da goyon bayan kafa rundunar ƴan sandan jihohi domin magance matsalolin tsaro a ƙasar nan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!