Connect with us

Siyasa

gwamnonin najeriya sun yi wata ganawa a abuja kan mafi karancin albashi

Published

on

Gwamnonin kasar nan sun yi wata ganawa a daren jiya a birnin tarayya Abuja wadda suka tattauna batutuwa da suka shafi mafi karancin albashi da rashin tsaro da ke addabar kasa da kuma wasu lamuran da ke alaka da ci gaban kasa.

Rahotanni sun ce ana saran gwamnonin za su kuma gana da shugaban hukumar aikawa da sakonnin ta kasa da kuma attorney Janar kuma kwamishinan shari’a game da batun dagin kasa na bai daya.

Haka zalika yayin taron, za su kuma zanta kan rashin jituwa da ke abkuwa tsakanin bangaren majalisa da kuma na zartaswa.

Kungiyar kwadago ta kasa NLC dai, ta bukaci gwamnatin tarayya da ta amince da naira dubu sittin da shida a matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikata, lamarin da kungiyar gwamnonin ke shakku kan hakan.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!