Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnonin PDP muna goyon bayan sake fasalta Najeriya – Tambuwal

Published

on

Gwamnonin jam’iyyar PDP sun goyi da bayan sake fasalta kasar nan don dakile matsalolin tsaro.

 

Gwamnonin sun dau wannan mataki ne yayin wani taron sirri da suka gudanar a yau litinin a Ibadan babban birnin jihar Oyo.

 

Haka zalika gwamnonin na PDP sun kuma bukaci shugaban kasa Muhammadu Buhari da ya fara shirye-shiryen samar da ƴan sandan jihohi don magance matsalolin tsaro da ke addabar Najeriya.

 

 

A yayin tattaunawar rahotanni sun ce gwamnonin sun tattauna al’amuran da suka shafi tabarbarewar tsaro da kuma koma baya da tattalin arzikin kasar nan ke fuskanta a wannan lokaci.

 

Matsayar gwamnonin na PDP na cikin wata takardar bayan taro ne mai dauke da sa hannun shugaban ƙungiyar gwamnonin na PDP kuma gwamnan jihar Sokoto Aminu Waziri Tambuwal.

 

A bangare guda gwamnonin na PDP sun goyi bayan matakin da takwarorinsu na kudu suka dauka na haramta kiwo da makiyaya ke yi barkatai a yankunansu.

 

Gwamnonin da suka halarci taron sun hada da: Aminu Waziri Tambuwal, (Sokoto), Udom Emmanuel, (Akwa Ibom), Douye Diri, (Bayelsa), Samuel Ortom, Benue State da kuma Ifeanyi Okowa na jihar (Delta).

 

Sauran sune: Ifeanyi Ugwuanyi, (Enugu), Nyesom Wike, (Rivers), Seyi Makinde, (Oyo), Ahmadu Fintiri, (Adamawa) da kuma Godwin Obaseki na jihar (Edo).

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!