Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Har yanzu ana ci gaba da binciken asalin corona – WHO

Published

on

Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce, har yanzu tana kan bakanta na ci gaba da bincike kan asalin samuwar cutar Korona da ta yi sanadiyyar mutuwar miliyoyin mutane tare da kassara tattalin arziƙin ƙasashe da dama.

Tuni Majalisar ɗinkin duniya ta ce, alhakin gudanar da binciken na kan masana kimiyya, inda ta ce, magance sake barkewar cutar ya ta’allaƙa ne idan an yi binciken.

Tuni tawagar hukumar lafiya ta duniya ta isa birnin Wuhan don ci gaba da binciken, duk kuwa da yadda China ke kokarin yi wa shirin ƙafar ungulu, a cewar WHO.

Najeriya ce ƙasa ta 4 a yaƙi da cutar corona a duniya – WHO

Ƙwararru sun zargi cewa cutar ta samo asali daga birnin Wuhan, sakamakon cin naman jemage, yayin da zarge-zarge suka fara ɓulla kan cewa an ƙirƙiri ƙwayar cutar a ɗakin gwaje-gwajen ƙwayoyin hallita.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!