Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Mun yiwa yara miliyan 100 rigakafin Polio a Afrika – WHO

Published

on

Hukumar lafiya ta duniya WHO ta ce, a kalla yara miliyan 100 a yankin Afrika, sun karɓi rigakafin cutar Polio a shekarar da ta gabata.

Shugaban hukumar a yankin Afrika Dr Matshidiso Moeti ne ya bayyana hakan, ta cikin wata sanarwa da ya fitar.

Ya ce, annobar corona ta ƙara ba da dama wajen gudanar da rigakafin cutar Polio, wanda ake hasashen hakan zai iya kawo ƙarshen cutar a yankin Afrika.

Har yanzu ana ci gaba da binciken asalin corona – WHO

A cewar sa, akwai buƙatar ba da haɗin kai ga WHO don isa yankunan da ba a yiwa yaran su rigakafin ba, duk da cewa afrika ta kai matakin fita daga ƙasashe masu fama da cutar, bayan da ta kwase shekara huɗu ba a samu rahoton masu ɗauke da cutar ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!