Connect with us

Labarai

Har yanzu ba a samu hanyar tuntubar wadanda suka sace masu ibada a jihar Neja ba

Published

on

Gwamnatin Jihar Niger ta ce har yanzu ba ta samu wata hanyar tuntubar wadanda suka sace masu ibada a jihar ba, kwanaki shida bayan harin da aka kai yayin sallar Juma’a.

Kwamishinan Yada Labarai na jihar, Obed Nuhu, ya ce har yanzu gwamnati ba ta tabbatar da adadin mutanen da aka sace ba.

Ya ce harin na ranar 21 ga Agusta ya faru a wurare uku daban-daban a Karamar Hukumar Borgu, kuma ana zargin mayakan Lakurawa da Boko Haram ne suka kai shi.

Kwamishinan ya ce gwamnati na ci gaba da tattara bayanai, don haka ba za ta yi amfani da alkaluman da ba a tabbatar da su ba.

Rahotanni sun ce ‘yan ta’addan sun kai hari kan masu ibada a masallacin Kpenya da ke Gidan-Zana, inda suka sace mata da yara da kuma tsofaffi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!