Labarai
Zan buɗe iyakokin Najeriya idan aka zaɓe ni a 2027 -Atiku Abubakar

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na 2027 a ƙarƙashin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), Atiku Abubakar, ya ce zai sake buɗe iyakokin ƙasar nan da ƙasashen makwabta idan aka zaɓe shi a matsayin shugaban ƙasa.
Atiku ya ce rufe iyakokin ya yi matuƙar shafar harkokin tattalin arziki a jihohin Arewa da ke makwabtaka da Kamaru, Chadi, Nijar da Benin.
Ya ce matasa da dama da ke dogaro da halastaccen kasuwancin ketare sun shiga matsananciyar wahalar kuɗi sakamakon takunkumin da aka sanya.
Ya ƙara da cewa sake buɗe iyakokin zai taimaka wajen farfaɗo da kasuwancin ketare tare da dawo da damar samun sana’o’i da kuɗaɗen shiga ga al’ummomin da abin ya shafa.
You must be logged in to post a comment Login