Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Har yanzu jihar Kano na mataki na 7 a jihohin da aka fi shaye-shayen kwayoyin maye – NDLEA

Published

on

Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta ƙasa ta cafke mutane 60 cikin kwanaki biyu da laifin tu’ammali da kwayoyin maye.

Hukumar reshen jihar Kano ta bakin shugaban hukumar Isah Likita ne ya tabbatar da hakan.

Ya ce “jami’an mu sun kama mutanen ne a guraren shan kayan maye, inda aka same su dumu-dumu suna sha kuna suna buguwa”.

Isah Likita ya kuma ce, hukumar ta samu bayanan sirri ta hanyar raba lambar waya ga al’umma.

“Abinda shugaban hukumar NDLEA ta kasa Janar Buba Marwa mai ritaya ke nufi, na cewa Kano ita ce ta farko da tafi kowace jiha tu’amali da miyagun ƙwayoyi shi ne, jihar ita ce tafi kowacce jiha yawan al’umma dalilin kenan da ya sa ake kallon masu sha suna da yawa.

Likita ya ƙara da cewa, jihar Kano har yanzu tana mataki na bakwai na masu shan ƙwayoyi.

 

 

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!