Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Har yanzu mata na fuskantar cin zarafi- Barrista Hussaina Aliyu

Published

on

Tsohuwar shugabar Kungiyar Lauyoyi mata ta kasa reshen jihar Kano Barrista Hussaina Aliyu tace har yanzu mata na cigaba da fuskantar matsalar cin zarafi a wajen maza wanda matsalar ke shafar su har a bangaren siyasa idan sun tsaya takara a siyasa.

Barrista Husaina Aliyu ta bayyana haka ne ta cikin shirin muleka mu gano na musamman na gidan Radio Freedom daya mayarda hankali kan bikin ranar mata ta duniya da majalisar dinkin duniya ta ware ranar sha uku ga watan Maris.

Husaina Aliyu Ibrahim tace abun takaicin ma ba iya nan matsalar ciwa mata zarafi ta tsaya ba harda cigaba da kiran sunan mace da wani suna mara dadin ji da maza keyi idan sun tsayawa takara ta siyasa a kowacce jam’iyya wanda hakan ke sanya rayuwar mata cikin damuwa.

Barista Husaina Aliyu Ibrahim ta nanata cewa mata a yanzu na fuskantar matsala musamman a bangaren zamantakewar su ta aure a wajen mazajen su wanda a yanzu matsalar ke cigaba da samun gindin zama a tsakanin su.

Wakilin mu Abdulkarim Muhammad Abdulkarim Tukuntawa daya bibiyi yadda shirin ya gudana ya ruwaito Tsohuwar shugabar kungiyar na cewa ko a bangaren daukar aiki ma ana barin mata a baya saka

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!