Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Hisbah ta ƙulla yarjejeniya da ƴan kasuwar Kwanar Gafan

Published

on

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta ƙulla yarjejeniya da ƴan kasuwar Gwari ta kwanar Gafan dake ƙaramar hukumar Garin Malam a nan Kano.

Hisbar ta ƙulla yarjejeniya da ƴan kasuwar ne domin yin aiki tare da jami’an ta wajen tabbatar da bin dokokin shari’a tare da kaucewa aikata baɗala.

A cikin wata sanarwa da mai taimakawa babban kwamandan Hisbah na jiha Bashir Muhammad Sani ya fitar a yau Lahadi ta ce, an ƙulla yarjejeniyar ne a yayin wata ziyara da tawagar hukumar ta kai kasuwar a yau.

Sanarwar ta ce, jami’an Hisbah bisa jagorancin babban kwamandan Malam Muhammad Harun Ibn Sina sun gana da shugabannin kasuwar inda suka tattauna batutuwa da dama tare da tunasar da ƴan kasuwar kan su ci gaba da yin kasuwanci tare da riƙo da gaskiya da kuma kyawawan halaye da addinin musulunci ya koyar.

Idan zaku iya tunawa dai tun a shekarun baya an sha kai ruwa rana tsakanin ƴan kasuwar da jami’an hukumar Hisbah kafin samun wannan yarjejeniya, domin ko a shekara ta 2012 an samu mummunan rikici wanda yayi sanadiyar raunata ƴan Hisbah sama da 40, inda su kuma ƴan Hisbah suka cafke mata masu zaman kan su sama da 89 a kasuwar.

Hotuna a yayin ziyarar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!