Connect with us

Labarai

NDLEA ta cafke tarin miyagun kwayoyi da aka boye a kayayyakin da aka shigo da su

Published

on

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa, NDLEA, ta ce ta cafke wasu tarin miyagun kwayoyi, wadanda aka boye a cikin kayayyakin da aka shigo da su Najeriya, a samamen da ta gudanar a wasu jihohin kasar nan.

Haka kuma, an gano wasu tarin miyagun kwayoyi guda biyu da aka boye a cikin lasifikokin kiɗa, inda aka cafke su a wasu tashoshin mota a Jihar Legas.

A cewar kakakin hukumar NDLEA, Femi Babafemi, akalla mutane bakwai da ake zargi da hannu wajen safarar miyagun kwayoyin, da jami’an hukumar suka kama a yayin samamen.

A wani samame da jami’an NDLEA suka gudanar a sashen ajiyar kayayyakin da ake shigowa da su kasar nan , na filin jirgin saman Murtala Muhammed da ke Ikeja a jihar Lagos, jami’an sun gano wani kaya da ake shirin aikawa zuwa Birtaniya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!