Connect with us

Labarai

Kano: Ƴan sanda sun kama mutane 248 da ake zargi da manyan laifuka

Published

on

Rundunar ƴan Sandan jihar Kano, ta ce, ta kama mutane 248 da ake zargi da hannu a aikata laifuka daban-daban da suka hada da fashi da makami, garkuwa da mutane, safarar miyagun kwayoyi da kuma tayar da tarzoma cikin wata guda.

Kwamishinan ƴan Sandan jiha Ibrahim Adamu Bakori, ne ya bayyana hakan yayin taron manema labarai da aka gudanar a hedikwatar rundunar da ke Bompai a nan Kano.

Ibrahim Adamu Bakori  ya ce, daga cikin wadanda aka kama akwai mutane 18 da ake zargi da fashi da makami, biyar masu garkuwa da mutane, 32 masu safarar miyagun kwayoyi, 12 masu satar motoci, 11 masu satar adaidaita sahu, shida masu satar babura da kuma wasu 15 da ake zargi da sata.

Ya kara da cewa, an kama mutane 149 da ake zargi da hannu a rikice-rikicen tarzoma da suka faru a sassa daban-daban na jihar

Rundunar ta ce ta kwato makamai masu hadari da dama da suka hada da bindiga kirar pistol guda daya, bindigogi da kera a gida guda hudu,da harsasai guda biyar da kuma addina guda 232 sai wukake 374 da gatari 13 kibiyoyi 23 da gororo 37 da sauran su

Haka kuma, kwamishinan ya buƙaci al’umma da su ci gaba da bai wa jami’an tsaro hadin kai ta hanyar bayar da bayanan sirri.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!