Labarai
Hukumar Kare Hakkin Masu Saye ta Kano ta kama magungunan kwari da wa’adin su ya kare

Hukumar kare Hakkin masu saye ta jihar kano KCPC, ta kama kimanin katan 419 na magungunan kwari da wa’adin amfani da su ya kare, a wani wuri da ke kan Titin Club Road a nan Kano.
Hukumar ta ce samamen ya biyo bayan samun bayanan sirri cewa an tara magungunan a wurin, tare da zargin cewa ana kokarin sauya musu yanayi ko mazubi domin sake mayar da su kasuwa.
Daraktan wayar da kai na hukumar, Jamilu Mustapha Yakasai, ya bayyana cewa jami’an hukumar sun rufe wuraren da ake ajiye magungunan, yayin da ake ci gaba da bincike domin daukar matakin doka.
Shugaban hukumar Dr. Ibrahim Garba Muhammad, ya kuma yi kira ga al’umma da su kasance masu sanya ido, tare da kai rahoton duk wani samfurin da suke zargin bai dace da amfani ba.
You must be logged in to post a comment Login