Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Hukumar kula da gidajen yari ta kasa ta ce ba gaskiya bane cewar fursunoni sun fasa gidan yari a Minna

Published

on

Hukumar kula da gidajen yari ta kasa, ta ce; ba gaskiya bane cewa fursunoni sun fasa gidan yarin garin Minna a makwan jiya.

 

A cewar hukumar, lamarin da ya faru a kwanakin baya hari ne kawai aka kai gidan yarin amma ba fursunoni ne suka fasa gidan yarin ba.

 

Mai magana da yawun hukumar Francis Enobore shi ya bayyana haka ga manema labarai jiya a Abuja.

 

Ya ce ya zama wajibi hukumar ta wayar da kan al’ummar kasar nan musamman wadanda ke cewa fursunoni ne suka fasa gidan yarin suka tsere.

 

A baya-bayan nan ne dai wasu ‘yan bindiga suka kai hari ga gidan yarin da ke garin Minna, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar wani jami’in hukumar daya da kuma wani mutum da ke tafiya akan babur kusa da gidan yarin.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!