Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

NDLEA ta fitar da sunayen kasashe 8 da ta ke bukatar su bada biza ga masu son zuwa kasashen

Published

on

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA ta bayyana sunayen wasu kasashe takwas da ta ke bukatar su ba da izinin biza ga wadanda ke da niyyar zuwa kasashen.

Kasashen sun hadar da: Thailand da Malaysia da Indonesia sai India da kuma Brazil da Philippines sai kasar Rasha.

Wannan dai na cikin wata sanarwa da daraktan yada labarai na hukumar ta NDLEA Mista Femi Babafemi ya fitar a jiya Laraba.

Sanarwar ta bayyana sunan kasashen don musanta zargin cewa tana gabatar da haraji ne ga matafiyan, tana mai cewa bukatar da aka gabatar daga kasashen takwas ba sabon abu bane domi kuwa an shafe tsawon shekaru 24 ana gudanarwa.

A cewar sanarwar wannan wani mataki ne da zai kara bai wa hukumar damar yakar masu safarar miyagun kwayoyi tsakanin kasashe.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!