Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

IAAF: An tura tsohon shugaban hukumar gidan gyaran hali

Published

on

Tsohon shugaban hukumar wasannin guje-guje da tsalle-tsalle ta duniya wato IAAF, Lamine Diack, an yanke masa hukuncin dauri a gidan gyaran hali sakamakon samun sa da hannu a aikata cin hanci da rashawa.

An dai zargi shugaban mai shekaru 87, da badakalar kudaden da suka shafi ta’ammali da miyagun kwayoyi a kasar Rasha.

Lamine Diack dan kasar Senegal, ya karbi kudade daga hannun ‘yan wasan kasar ta Rasha don yin rufa-rufa, sakamakon samun su da laifin amfani da kwayoyin kara kuzari da kuma kyale su ci gaba da wasanni Olympics na shekarar 2012 da aka gudanar a birnin London.

Mahukuntan kasar Faransa da suka gudanar da bincike akan zargin ne, suka yanke wa tsohon shugaban hukuncin daurin shekara 4 a gidan gyaran hali tare da biyan tarar Yuro 500,000.

Haka zalika, lauyan dake kare tsohon shugaban ya ce basu gamsu da wannan hukuncin ba, yana mai cewa za su daukaka kara zuwa kotu ta gaba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!