Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

ilimi

Idan ana son zaman lafiya a biya mu haƙƙinmu – ASUU

Published

on

Ƙungiyar malaman jami’o’i ta ƙasa ASUU ta ce, idan ana son zaman lafiya a biya ta haƙƙi mambobinta na wata 8.

Kalaman ASUU na zuwa ne a matsayin martani ga gwamnatin tarayya biyo bayan fara biyan mambobin sabuwar ƙungiyar malaman jami’o’i ta CONUA albashin wata 8.

Da yake yiwa Freedom Radio ƙarin bayani, shugaban ASUU shiyyar Kano, Farfesa Abdulkadir Muhammad ya ce, rashin biyan su albashinsu ba zai hana su ɗaukan mataki na gaba ba.

 

Muna da matakai daban-daban da za mu ɗauka, ba iya yajin aiki ba, amma zaman lafiya shi ne a biya mu a haƙƙinmu”.

Ya ci gaba da cewa “Haƙƙin mu ne a biya mu albashin wata 8 na yajin aiki, in har ana son wanzuwar zaman lafiya, don haka duk matakin da muka ɗauka a nan gaba kar ayi mamaki”.

A baya-bayan nan ne rahotanni suka nuna cewa, gwamnatin tarayya ta fara biyan albashin wata 8 ga mambobin ƙungiyar CONUA na lokacin da suka yi yajin aiki.

Idan za a iya tunawa gwamnatin tarayya ta yiwa ƙungiyar CANUA rijista a lokacin da ƙungiyar ASUU ke tsaka da yajin aiki, wadda kuma ake sa ran za ta maye gurbinta.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!