Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kaduna

Inconclusive: Kotu ta umarci a sake zaɓe a jihar Kaduna

Published

on

Kotun sauraren ƙararrakin zaɓe da ke zamanta a Kaduna, ta bayyana zaben gwamnan jihar na 2023 a matsayin wanda bai kammala ba.

Kotun ta yi hukunci ne a zamanta na ranar Alhamis inda ta bayyana zaɓen a matsayin wanda bai kammala ba tare da bayar da umarnin sake gudanar da wani zaɓen ga hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa INEC cikin kwanaki 90.

Tawagar alƙalan su uku ƙarƙashin jagorancin mai shari’a Victor Oviawe, ya bayar da umarnin sake gudanar da zaɓe a rumfunan zabe 24 da ke gundumomi bakwai na ƙananan hukumomi huɗu da suka kunshi masu rajista 16,300.

Zaman yanke hukuncin dai ya gudana ta kafar Zoom, bayan alkalan sun kaurace wa zauren taron.

Idan za a iya tunawa jam’iyyar PDP da dan takararta Isah Mohammed Ashiru ne suka shigar da ƙarar, suna ƙalubalantar nasarar Sanata Uba Sani na jam’iyyar APC bisa zargin maguɗin zaɓe.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!