Labarai
INEC ta amince da tsawaita wa’adin ci gaba da rajistar katin zabe

Hukumar zabe ta Kasa INEC, ta amince da tsawaita wa’adin ci gaba da rajistar masu kada kuri’a (CVR) da karin makwanni biyu.
A baya dai an tsara kammala rijistar ne a ranar 10 ga watan Yuli, 2026, amma hukumar ta ce yanzu za a ci gaba da yin rijistar har zuwa ranar 24 ga watan na Yuli.
Hukumar ta bayyana cewa ta dauki wannan mataki ne bayan bukatar da dimbin ‘yan Najeriya masu cancantar kada kuri’a suka gabatar, domin ba wa karin mutane damar yin rajista da kuma tabbatar da cewa babu wanda ya rasa damar shiga cikin kundin masu kada kuri’a kafin zabuka masu zuwa.
INEC ta ce wannan tsawaitawa na nuna kudirinta na tabbatar da cewa duk wani dan Najeriya da ya cika sharuddan yin zabe ya samu dama cikin sauki wajen yin rajista, domin karfafa tsarin dimokuradiyya da kuma fadada shigar al’umma cikin harkokin zabe a fadin kasar.
You must be logged in to post a comment Login