Connect with us

Labarai

Yanzu yanzu: INEC ta sanya ranar zaben shekarar 2023

Published

on

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta sanya ranar 18 ga watan Fabarairun shekarar 2023 a matsayin ranar da za a gudanar da babban zaben kasa.

Shugaban hukumar Farfesa Mahmud Yakubu ne ya  sanar da hakan yau, lokacin da yake jawabi a gaban kwamitin majalisar dattijai kan hukumar INEC, kan yadda za a samar da hukumar kula da laifuffukan da aka aikata lokacin zabe.

Farfesa Mahmud Yakubu ya ce bayan shafe tsawon shekaru 13 ana tattaunawa kan shawarwarin da Justice Muhammad Uwais ya bayar don samar da hukumar kula da laifukan zaben, yanzu haka dai sun kawo wannan gaba.

Ya kara da cewa a zaben shekarar 2015, sun karbi korafe-korafe 124 inda ya zuwa yanzu aka zartar da hukunci a kan guda 60.

Tun da fari shugaban kwamitin majalisar dattijan Sanata Kabiru Ibrahim Gaya, ya ba da tabbacin cewa kudurin dokar zai samu sahalewar shugaban kasa Muhammadu Buhari bayan sun kammala amincewa da shi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!