Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Addini

Inyass ya tabbatar wa Muhammadu Sanusi na 2 jagoranci Ɗarikar Tijjaniya a Najeriya

Published

on

Jagoran ɗarikar Tijjaniya na duniya Sheikh Muhammadul Mahi Inyass, ya tabbatar wa Sarkin Kano na goma sha hudu a daular fulani, Malam Muhammadu Sanusi na biyu mukamin jagoran ɗarikar Tijjaniya a Najeriya.

 

Mai magana da yawun tsohon gwamnan babban bankin kasa (CBN) Sa’adatu Baba Ahmad ce ta sanar da hakan ta cikin wani sako da ta wallafa a shafinta na facebook a yau litinin.

 

Ta ce shugaban ɗarikar Tijjaniya ta duniyar ya tabbatar wa Malam Muhammadu Sanusi na biyu jagoranin Tijjaniyar ce a garin Madina Baye Kaulaha da ke kasar Senegal, bayan kammala sallar asham a jiya lahadi.

 

Tun bayan rasuwar tsohon jagoran ɗarikar marigayi Sheikh Khalifa Isyaku Rabi’u a shekarar 2018, ɗarikar ta Tijjaniya ba ta nada sabon shugaba ba.

 

Idan za a iya tunawa ko da kakan sarkin na goma sha hudu wato Muhammadu Sanusi na daya ya rike mukamin na jagoran ɗarikar Tijjaniya

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!