Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Jakadan Najeriya a kasar Chadi ya buya sakamakon barazana ga rayuwarsa

Published

on

Jakadan Najeriya a kasar Chadi Muhammad Dauda ya buya sakamakon barazana da rayuwarsa da ya ce ana yi tun bayan ba’asin da ya bayar gaban kwamitin Majalisar Wakilai, kan badakalar da ake zargin ta wakana a hukumar leken asiri ta kasa NIA.

Jaridar Premium Times ta wallafa a shafinta na Intanet cewa gwamnatin tarayya ce ta baiwa Jakadan rikon kwaryar kujerar babban daraktan NIA sakamakon dakatar da mai rike da mukamin Ayo Oke da aka yi, bisa zargin badakalr kudade, domin samun damar gudanar da bincike.

Muhammad Dauda ya rike mukamin ne daga watan Nuwamban bara zuwa watan Janairun bana, kafin maye gurbinsa da Ahmad Rufa’i Abubakar

Daga bisani aka sake maida shi kan kujrearsa ta Jakadancin kasar nan a Chadi, amma ya yi ikirarin cewa rayuwarsa tana fuskantar barazana.

A jawabin da ya gabatar yayin bada ba’asi gaban kwamitin bincike na Majalisar Wakilai, Ambasada Muhammad Dauda ya zargi shugaban kwamitin da shugaban kasa ya kafa domin bincikar badakalar hukumar ta NIA Babagana Kingibe da hannun cikin wata almundahanar kudi.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!