Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

ilimi

Cacar baki: JAMB ta yiwa El-rufa’i martani

Published

on

Hukumar shirya jarrabawar shiga manyan makarantin ƙasar nan JAMB ta ce bata bayar da fifikon maki ga ɗaliban da suka rubuta jarabawar a yankin arewacin ƙasar nan.

Hukumar ta kuma ce gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, bai yi daidai ba da ya ce ana sangarta ɗaliban Arewa da maki  fiye da na yankin Kudancin ƙasar nan.

Shugaban sashinyaɗa labarai na hukumar JAMB, Fabian Benjamin ne ya bayyana hakan a wata hira ta musamman da jaridar PUNCH.

Wannan dai ya biyo bayan kalaman gwamnan Kaduna Nasir El-Rufai da yayi a cikin shirin gidan Talabijin na Channels ranar Litinin, inda ya ce bai kamata a riƙa fita maki ga yan Arewa fiye da takwarorin su na kudu ba, domin kuwa zai kara musu lalaci.

Benjamin ya ce JAMB ba ta taɓa saka mafi ƙarancin maki ga makarantu ba tun lokacin da aka kafa ta a shekarar 1978 a matsayin hukumar da za ta riƙa shirya jarrabawar bai wa dalibai damar shiga manyan makarantu a ƙasar nan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!