Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Jami’an tsaro ku kama duk mai tunzura jama’a-Sarkin musulmi

Published

on

Sarkin Musulmi

Shugaban majalisar koli ta addinin musulunci kuma Sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar, ya bukaci jami’an tsaron  kasar nan da su dauki matakin kama duk wami malamin addini da ke yada kalaman tunzura jama’a.

Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar ya bayyana hakan ne yayin wani taron zaman lafiya da kuma gina kasa, da majalisar Da’awah ta kasa ta shirya a garin Jos babban birnin jihar Plateau.

Ya ce, akwai bukatar a rika gudanar da harkokin addinai ta yadda za a kaucewa tada rikice-rikice.

Matsalolin aure: Sarkin Kano ya bukaci a koma makaranta

Abinda ya sa ban ce komai ba kan batun sanya Hijab a Jamia: Sarkin Musulmi

Sarkin musulmi ya bukaci gwamnatin tarayya ta zage dantse don magance matsalolin tsaro

Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar ya kuma yi kira ga kungiyar Jama’atu Nasril Islam da kungiyar Kiristoci ta kasa CAN da su yi dukkan mai yiwuwa wajen kawo karshen cece-kucen dake faruwa tsakanin mabiya addinan biyu a kafafen yada labarai.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!