Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Jami’ar NOUN ta gargadi dalibai masu takarardun bogi

Published

on

Jami’ar Karatu daka gida ta ja hankalin dalibai da jami’an tsaro da sauran al’umma gaba daya kan takardun jarrabawar na bogi da ke yawo a kafafen sadarwa na zamani da ke ake zargin daga hukumar makarantar suka fito.

 

Jami’in yada labaran Jami’ar ta NOUN Ibrahim Sheme ne ya bayyana haka a jiya Laraba a birnin tarayya Abuja.

 

Inda ya ce babu wata takardar jarrabawar da ta fito daga hukumar makarantar a hukuman ce ya kuma bukaci al’umma da su kaucewa batun.

 

Ya kuma ce jama’ar na iya kokarin ta wajen ganin ta girmama kanta da kare martabarta a idon duniya daga dukkanin irin wadannan abubuwan da ke faru da basu da tushe ballantana makama.

 

Sheme ya kara da cewa jami’ar ta NOUN ta shigar da korafi a rubuce ga hukumomin tsaro, inda ta bukaci  jami’an tsaron su bankado wanda ke da hannu kan wajen yada bayanan domin gurfanar da shi a gaban kuliya.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!