Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Sabon shugaban jami’ar NOUN ya kama aiki

Published

on

Sabon shugaban Jami’ar karatu daga gida NOUN Farfesa Olufemi Peters ya kama aiki a jiya alhamis, bayan da Farfesa Abdallah Uba Adamu ya kammala aikinsa na shekaru biyar yana jagorantar makarantar.

 

Wata sanarwa da daraktan yada labaran Jami’ar Ibrahim Sheme ya fitar, ta ce an gudanar da kwarya-kwaryar bikin karbar aikin jiya a shelkwatar NOUN din da ke birnin tarayya Abuja.

 

Farfesa Olufemi Peters shi ne shugaban Jami’ar na biyar, ya kuma bayyana tsohon shugaban makarantar Farfesa Abdallah Uba Adamu a matsayin jagora na gari da ya dora Jami’ar a kan tafarkin da ya dace na ci gaban ilimi.

 

A jawabinsa na ban kwana, shugaban Jami’ar mai baring ado Farfesa Abdallah Uba Adamu, godiya ya yi ga Ubangiji da ya ba shi damar shugabantar makarantar, tare da yi wa sabon shugaba fatan smaun nasara yayin jagorancinsa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!