Labarai
Jam’iyyar PDP ta kafa kwamitin da zai shirya babban taronta na kasa

Jam’iyyar PDP ta kafa kwamitin da zai shirya babban taron ta na kasa karkashin gwamman jihar Adamawa Amadu Fintiri.
PDP ta ce majalisar zartarwar ta amince da kafa wani karin kwamitin da zai yi nazari a kan tsarin karba karban mukamai a jam’iyyar gabanin babban taronta, a karkashin Gwamnan jihar Bayelsa Douye Diri.
Jamiyyar ta dauki wannan mataki ne a yayin zaman majalisar koli da ta gudanar a ranar Talata a Abuja.
A yayin taron, jam’iyyar ta kuma yi Alla-wadai da rufe shelkwatarta da hukumar kula da birnin Abuja ta yi, tare da shan alwashin bin kadin matakin.
A ranar Litinin hukumar kula da birnin Abuja, ta garkame shelkwatar PDP da aka fi sani da Wadata Plaza saboda rashin biyan haraji.
You must be logged in to post a comment Login