Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Ƙetare

Juyin mulki: ƙasashen larabawa sun buƙaci mayar wa farar hula mulki a Sudan

Published

on

Ƙasashen Saudiyya da Hadaddiyar Daular Larabawa sun bi sahun kawayensu na ƙasashen yamma wajen kira ga sojin ƙasar Sudan da suka karbe iko da su gaggauta mayar da mulki ga gwamnatin farar hula.

Wannan dai na zuwa ne bayan da a baya ƙasashen na larabawa da ke da kyakykyawar alaƙa da dakarun sojin Sudan ɗin, ba su yi wata kwakkwarar magana a kan karbe ikon da soji suka yi a kasar ba.

A sanarwar hadin gwiwa da suka fidda, sun bukaci da a gagauta sakin duk wadanda ake tsare da su sakamakon juyin mulkin, da ma janye dokar ta bacin da sojin suka saka a kasar.

Haka zalika, Kasar Amurka ta bukaci Hadaddiyar Daular Larabawa da ta kara matsa kaimi ga sojojin Sudan din da su saki hambararen firaminista Abdallah Hamdok daga daurin talala da suke ci gaba da yi masa a gida.

Al’ummar kasar Sudan na adawa da matakin karbe iko da sojojin suka yi, lamarin da ya kai su ga hawa tituna domin zanga-zangar lumana da ta yi sanadiyar rasa rayukan wasu daga cikinsu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!