Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Tsohon gwamnan bankin CBN ya ce kamata yayi a samar da asusun tallafawa kananan masana’antu

Published

on

Tsohon gwamnan babban bankin kasa CBN Farfesa Kingsley Moghalu ya bayyana cewa kamata yayi a samar da wani asusu da zai tara kudade da yawan su ya kai biliyan 500 don habaka kanana da matsakaitan masana’antu da nufin bunkasa tattalin arzikin kasar nan.

Kingsley Moghalu wanda shugaban kungiya ce mai rajin samar da ingantaccen shugabanci da tattalin arziki, ya ce samar da asusun wanda za’a rika tara kudaden ne ta hanyar kamfanoni masu zaman kansu zai taimaka wajen habaka kanana da matsakaitan masana’antu tare da ciyar da tattalin arzikin kasar nan gaba.

Farfesa Kingsley ya bayyana hakan ne a yayin wata tattaunawa da Freedom Radio, inda ya kuma ce kasashe da dama sun habaka tattalin arzikin su ta hanyar samar da makamancin wannan asusu.

 

Ya kuma danganta matsalolin da kanana da matsakaitan masana’antu a Najeriya ke fuskanta da rashin isassun kudaden tafiyar da su da kuma karancin ilimin tafiyar da su.

 

Har-ila-yau ya kuma ce naira Biliyan Biyar da gwamnati ta ware wa bangaren tare kuma da naira dubu biyar da aka alkawarta baiwa matasan kasar nan cikin wannan kudi, ba zai samar da wani sauyin da ake bukata ba, domin kuwa yawan kudin bai kai mizanin yadda zai yaki talauci cikin al’umma ba

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!