Labarai
Kaduna: Yan Sandan sun tabbatar da kashe ‘yan bindiga 2 tare da kama 16

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kaduna ta tabbatar da kashe ‘yan bindiga biyu tare da kama wasu 16 a wani samame da ta gudanar.
Hakan na kunshe a cikin sanarwar da Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar, DSP Mansir Hassan, ya fitar.
Sanarwar ta bayyana cewa rundunar ta kuma kama mutane shida kan zargin buga jabun dalar Amurka.
Ya ƙara da cewa jami’an sun ƙwato bindigogi 10 da sauran manyan kayan da ake zargin ana amfani da su wajen aikata laifuka daban -daban.
You must be logged in to post a comment Login