Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya kaɗa ƙuri'arsa a mazaɓarsa ta Ganduje da ke ƙaramar hukumar Dawakin Tofa.
Gwamnan ya bi layi har yazo kansa sannan ya kaɗa ƙuri'arsa.
A mazaɓar an ɗauki matakan kariya na wanke hannu da sinadari saboda cutar Korona.
Wakiliyar mu Zahra'u Nasir ta ce, an samu dandazon al'umma a mazaɓar da suka fito domin kaɗa ƙuri'a.
Sai dai ba a samu bayar da tazara a tsakanin juna ba.
You must be logged in to post a comment Login
You must log in to post a comment.