Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ba zamu soke sakamakon mazaɓun da yara suka kaɗa ƙuri’a ba -KANSIEC

Published

on

Shugaban hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Kano Farfesa Garba Ibrahim Sheka ya ce, hukumar ba za ta soke sakamakon zaɓukan yankunan da aka samu rahotannin kananun yara suna kaɗa kuri’a ba.

A cewar sa, tun farko hukumar ta shaidawa jam’iyyu cewa su sanar da jamian tsaro a duk lokacin da suka ga ƙananan yara suna kaɗa kuri’a don ɗaukar matakin da ya dace.

Ya ce, zuwa yanzu rahotannin da hukumar ke samu zaɓe na tafiya lami lafiya sai dai ɗan abin da ba a rasaba.

Da aka tambaye shi game da rashin kaɗa ƙuri’a a kan lokaci, ya ce a rahotannin da suka samu kayyakin zaɓe sun isa rumfunan zaɓe a kan lokaci, wurare kaɗan ne aka samu akasi.

Farfesa Garba Ibrahim Sheka ya kuma ce, hukumar za ta ci gaba da sanya idanu don ganin an kammala zaɓen bisa ƙa’ida.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!