Connect with us

Labarai

Kano: Yan Bindiga sun hallaka wata mata tare da sace mutane 3 a Tsanyawa

Published

on

‘Yan Bindiga sun hallaka wata mata tare da yin garkuwa da mutane uku a kauyen ‘Yan kamaye dake karamar hukumar Tsanyawa a daren jiya Asabar.

Jaridar Daily Nigerian ta ruwaito cewa ‘yan bindigar sun shiga garin ne da misalin karfe 11 na daren jiya Asabar lokacin da al’ummar garin kowa ya kwanta Bacci.

Rahotanni sun tabbatarwa da jaridar cewa ‘yan ta’addan sun ajiye Baburan da suka taho da su a bayan gari, inda suka shiga da kafa don gudun hayaniya.

A cewar majiyar, maharan sun harbi wata Dattijuwa dake kokarin dakatar da su bayan da ta rika rokon su kan kada su tafi da danta.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!