Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Kano zata hada kafada da kasashen duniya a bangaren ilimi –Ganduje

Published

on

Gwamnatin jihar Kano, ta sha alwashin bunkasa harkokin ilimi dana lafiya, don yin kafadu da takwarorin su na kasashen duniya, kasancewar su su ne kashin bayan cigaban dukkan wata al’umma, jiha ko kasashe.

Gwamnan jihar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana haka a yayin wani taron daya gudana a gidan gwamnati da manyan sakatarorin da manyan jami’an gwamnati don dubawa da kare kasafin kudin shekara ta dubu biyu da ashirin, na ma’aikatu daban daban na jiha.

Gwamna Abdullahi Umar Ganduje, ya ce duk da cewar wasu bangarori na da matukar muhimmanci musamman ma bagaren Noma da kuma harkokin tsaro, gwamnatin sa zata bada fifiko ne wajen Ilimi, da harkar lafiya don haka ta fito da tsarin yin ilimi kyauta kuma wajibi.

Tun da fari da yake jawabi shugaban ma’aikata na jihar Kano, Dr Kabir Shehu yace sun zo ne don gabatarwa tare da kare kasafin kudaden shekarar ta 2020, na ma’aikatu daban -daban dake jihar nan.

Wakilinmu Aminu Halilu Tudunwada, ya ruwaito mana cewa, gwamna Ganduje ya yi alkawarin gabatar da yan majalisar zartawar wa wato kwamishinoni nan ba da dadewa, don su gudanar da ayyukan da kasafin kudin ya kunsa na ma’aikatun su daban -daban don cigaban jihar da kuma al’ummar ta.

RUBUTU MASU ALAKA:

Yaran Kano 9: Ganduje ya kafa kwamitin bincike na musamman

Yaran da aka sace sun kaiwa Ganduje ziyara

Ganduje yayi Allah wadai da masu sace mutane

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!