Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

KAROTA ta kai sumame Gandun Albasa

Published

on

A daren jiya Litinin ne hukumar lura da zirga-zirgar ababen hawa ta Kano wato KAROTA ta kwashe kayayyakin ƴan kasuwar sayar da kujeru da kayan katako da ke unguwar Gandun Albasa a nan birnin Kano.

Wani mai sayar da kujeru a wurin ya shaida wa Freedom Radio cewa jami’an KAROTA sun yiwa titin ƙawanya cikin dare tare da kwashe kayayyakin ƴan kasuwar da ke bakin titi suka kuma tafi da su.

‘Yan kasuwar dai sun ce dama hukumar Karota ta basu wa’adin su matsar da kayayyakin su daga bakin titi, kuma suka bi umarnin amma duk da haka sai ‘yan Karotan suka je gurin tare da kwashe kayan.

Alhaji Nasiru Usman Na’ibawa shi ne mai bai wa gwamnan Kano shawara kan hukumar ta Karota yace hukumar na da hurumin aiki a ko ina, musamman tabbatar da cewa masu sana’o’I basu cushe hanyoyin wucewar jama’a ba.

Ya ce bisa al’ada idan hakan ta faru shugabannin kasuwa kan je hukumar don karbar kayan mambobin su amma bisa sharadin daina kasa kaya barkatai a kan titi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!