Labarai
KAROTA ta zargi wasu matasa da kai wa jami’anta hari tare da kona motar aiki

Hukumar Kula da Zirga-zirgar ababen Hawa ta Jihar Kano KAROTA ta zargi wasu fusatattun matasa da kai wa jami’anta hari tare da kona motar aiki a yankin Kwanar Dawaki.
Hukumar ta bayyana cewa, hakan ya faru ne biyo bayan wani hatsarin mota da ya afku tsakanin wata babbar motar daukar Kaya da wata motar kirar Sharon.
Mataimakin Shugaban Hukumar ta KAROTA, Auwal Shu’aibu Aranposu, ne ya bayyana hakan ga Freedom Radio ta wayar tarho.
Ya ce, lamarin ya faru ne yayin da jami’an hukumar ke tsaka da gudanar da aikinsu na kula da zirga-zirga ababen hawa.
You must be logged in to post a comment Login