Labarai
Katsina: Yan sanda sun ceto mata 2 da aka yi garkuwa da su

Rundunar ‘Yan sandan Jihar Katsina ta ceto wasu mata biyu da aka yi garkuwa da su tare da daƙile yunƙurin satar Shanu a ƙananan hukumomin Kankia da Charanchi.
Hakan na cikin sanarwar da mai magana da yaun runduna, ASP Abubakar Sadiq Aliyu, ya fitar.
Sanarwar ta bayyana cewa dakarun rundunar sun yi artabu da ƴan bindiga bayan sun kai hari ƙauyen Jauga da ke Sabon Gida a Ƙaramar Hukumar Kankia, lamarin da ya sa suka tsere zuwa daji tare da barin matan biyu da suka yi garkuwa da su.
Matan da aka ceto sun haɗa da Rukayya Yahaya mai shekara 20 da Sahura Abdulhadi mai shekara 22.
Rundunar ta ƙara da cewa a wani samame daban, ta daƙile yunƙurin satar shanu da ƴan bindiga suka kai ƙauyen Majen Waya da ke Ƙaramar Hukumar Charanchi bayan musayar wuta da aka yi tsakaninsu da jami’an tsaro.
Sanarwar ta ce, babu wanda ya rasa ransa kuma ba a yi nasarar sace ko guda daga cikin shanun ba, yayin da ake ci gaba da farautar ƴan bindigar.
You must be logged in to post a comment Login