Connect with us

Labarai

Kebbi: Sojoji sun ƙwato tarin manyan makamai daga hannun ƴan bindiga

Published

on

Dakarun Sojin kasar nan na Fansan Yamma da ke aiki a Jihar Kebbi, sun kwato tarin manyan makamai da kuma bama-bamai a ci gaba da ƙoƙari da nufin kawar da ta’addanci da sauran ayyukan miyagun laifuka a yankin Arewa maso Yamma.

Rahotonni sun bayyana cewa, an gudanar da wannan farmakin ne a yankin Dogon Daji da ke Ƙaramar Hukumar Dandi ta jihar, da ya yayin farmakin, jaruman dakarun sun yi amfani da ƙarfi wajen murƙushe ƙungiyar ‘yan ta’addan Lakurawa, lamarin da ya tilasta musu tserewa daga wajen.

A ci gaba da bin sawun ‘yan ta’addan da suka gudu ya kai ga gano da kwato dimbin makamai, bama-bamai da kayan aiki da suka bari a baya yayin tserewar su.

Mai magana da yawun rundunar, Laftanar Kanal Olaniyi Osoba, ya ce, kayan da aka kwato daga sansanin ‘yan ta’addan sun haɗa da bututun harba roka RPG da makaman rokokin yaƙi da dama da ake sama bututun harba roka da bama-bamai na gida masu yawa sai babura guda biyu da ‘yan ta’addan ke amfani da su wajen kai hari da caja ta batura, da wasu sauran kayayyaki.

Ya kuma ce, rundunar Sojin kasar nan za ta ci gaba da matsa lamba kan wadannan miyagun, tare da hana su damar gudanar da ayyukan su domin tabbatar da tsaro da lafiyar al’umma masu bin doka.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!