Connect with us

Ƙetare

An saka dokar hana fita sakamakon ɓarkewar zanga-zanga a yayin zaɓen shugaba kasa a Tanzaniya

Published

on

Rundunar yan sanda a ƙasar Tanzania sun saka dokar hana fita a fadin ƙasar baki daya biyo bayan zanga-zangar da ta ɓarke yayin zaɓen shugaban ƙasa da ya rikiɗe zuwa rikici da fadace-fadace a wasu sassan  ƙasar.

Rahotanni sun nuna cewa, zanga-zangar ta ɓarke ne a birnin Dar es Salaam da wasu garuruwa yayin da jama’a ke nuna rashin jin daɗi kan yadda ake gudanar da zaɓen shugaban ƙasar.

Masu zanga-zangar sun yi zargin cewa akwai son kai da rashin gaskiya a tsarin zaɓen, tare da neman gwamnati ta gyara tsarin zaɓe da kuma ba kowa damar faɗar albarkacin baki.

Jami’an tsaro, sun ce an sanya dokar ne domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Sai dai wasu ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan adam sun bayyana damuwa tare da bayyana hakan a matsayin tauye  ’yancin jama’a musamman a lokacin da ake jiran sakamakon zaɓen shugaban ƙasa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!