Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kotu ta bada umarnin aikewa da abduljabbar Kabara asibitin Dawanau

Published

on

Babbar kotun shariar musulinci dake ƙofar kudu karkashin mai sharia Ibrahim Sarki Yola ta bada umarnin a kai malam Abduljabbar zuwa asibitin Dawanau domin a duba lafiyar ƙwaƙwalwarsa da kuma kunnansa.

A zaman kotun na yau, kotun ta bada umarnin a karantawa malam Abduljabbar laifukan da ake tuhumarsa amma yaƙi amsawa.

Haka kuma lauyoyinsa sun ƙiyin martani kan tuhume tuhumen da ake masa a zaman na yau.

Mai sharia Sarki Yola ya bada umarnin a rubuta kwafin shari’ar baki ɗaya a baiwa lauyoyin Abduljabbar ɗin a nan take.

Sarki Yola na cewa koda lauyoyin malam Abduljabbar Kabara sun ɗaukaka ƙara ba za ta dakatar da ci gaba da shari’arsa ba.

Haka kuma ya sanya ranar 16 ga watan da muke ciki domin ci gaba da shari’ar.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!