Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kotu ta yankewa wani matashi hukuncin kisa a Zamfara

Published

on

Babbar kotun jiha ta daya dake birnin Gusau na jihar Zamfara ta yankewa wani matashi mai suna Kamalu Yusuf mazaunin unguwar Geji dake Gusau hukuncin kisa ta hanyar rataya.

Tunda farko dai ‘yan sanda ne suka gabatar da wanda ake zargi a gaban kotun bisa tuhumar aikata laifukan hada baki wajen aikata fashi da makami da kuma hallaka mahaifiyarsa Hajiya Hafsat Muhammad da kannensa Maryam Yusuf da Amina Yusuf har lahira a shekara 2013.

Wakilin mu a Zamfara Abdullahi Salisu Faru ya rawaito mana cewa ‘Yan sanda sun gurfanar da matashin Kamalu Yusuf tare da wani matashin mai suna Armaya’u Shehu, sai dai masu kara basu iya kawo kwararan shaidu akan shi Armaya’un ba.

Saboda haka ne babbar mai shari’a ta jihar Zamfara Hajiya Kulu Aliyu Gusau wadda ta jagoranci shari’ar ta sallami Armaya’un sannan ta yankewa Kamalu Yusuf hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan da aka sameshi dumu-dumu da hannu wajen aikata laifukan.

Karin labarai:

Rahoto: Kan dalilan da ya sanya ake yawan samu kisan kai a tsakanin ma’urata

Kotu ta yankewa matashi hukuncin kisa a Kano

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!