Labarai
Kotu ta yanke wa mutane biyu hukuncin kisa bisa yin garkuwa da jami’in NYSC

Babbar Kotun Jihar Ekiti ta yanke wa wasu mutane biyu, Ibrahim Abubakar da Abdullahi Abubakar, hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan ta same su da laifin yin garkuwa da wani jami’in Hukumar NYSC, Omoboade Adesina.
Kotun ta ce, an tabbatar da laifinsu ba tare da wata shakka ba, yayin da ta wanke mutum na uku, Usman Abubakar, saboda rashin isassun hujjojin da suka danganta shi da laifin.
Yayin da yake yanke hukunci, Alkalin Alkalan Jihar Ekiti, Mai Shari’a Lekan Ogunmoye, ya bayyana cewa shaidar tantance wadanda ake zargi da kuma bayanan kiran waya da aka tantance, sun taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da cewa Ibrahim da Abdullahi ne suka aikata laifin.
Saboda haka kotun ta yanke musu hukuncin kisa ta hanyar rataya, yayin da ta sallami tare da wanke Usman Abubakar daga dukkan tuhume-tuhumen da ake masa.
You must be logged in to post a comment Login