Labarai
Hukumar FRSC ta fara shirin daukar ma’aikata

Hukumar Kiyaye Hadurra ta Kasa, FRSC, ta ce, za ta fara daukar ma’aikata na shekarata 2026 don ciki guraben da dama a hukumar wanda dama ce ga yan kasa.
Wannan na cikin wata sanarwar da hukumar ta fitar mai sanye da sa hannun Mataimakiyar Shugabar Hukumar mai kula da harkokin gudanarwa Pauline Olaye.
Ta cikin sanarwar, hukumar ta ce, ana neman cike gurabe daban-daban domin kara karfin hukumar da nufin inganta ayyukanta a fadin kasar nan.
Hukumar ta bayyana cewa ana neman masu neman aiki a gurabe da dama daga ciki kuwa akwai Assistant Route Commander da kuma Marshal Inspector na biyu da na uku, tare da Road Marshal Assistant na daya, na biyu da na uku.
Hukumar ta kuma ce, masu neman mukaman jami’ai dole ne su kasance sun kammala jami’a ko kuma kwaleji ko cibiyoyin da gwamnati ta amince da su, yayin da masu neman sauran mukamai za su cika sharuddan ilimi da kwarewar da aka tanada ga kowane rukuni.
Hukumar ta kuma ce masu sana’o’i da direbobi za su iya neman aiki a karkashin sashin Road Marshal Assistant.
Ta kara da cewa dole ne mai neman aiki ya kasance dan Najeriya kuma ya iya amfani da kwamfuta, kuma ya kasance cikin koshin lafiya sannan a tanadi lasisin tuki da sauran abubuwan da aka bukata.
You must be logged in to post a comment Login