Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kotun ɗa’ar ma’aikata ta sanya ranar da za ta yanke hukunci tsakanin gwamnatin tarayya da kungiyar NARD

Published

on

Kotun ɗa’ar ma’aikata ta ƙasa ta saka ranar jumma’a 17 ga watan Satumba a matsayin ranar da zata yanke hukuncin ƙarar da gwamnatin tarayya ta kai ƙungiyar likitoci masu neman ƙwarewa.

Ƙarar dai ta biyo bayan yajin aikin da ƙungiyar ke gudanarwa sama da wata guda.

Mai shari’a Bashar Alkali, ne ya saka ranar ne biyo bayan sauraron duka bangarori biyu da ƙorafin da suka shigar dangane da taƙaddamar da ta barke tsakanin su akan yajin aikin da ƙungiyar ta tafi, da kuma batun babu aiki babu biyan albashi.

Da yake gabatar da jawabi Alƙalin ya buƙaci bangarorin biyu da su zauna a teburun shawarwari don samun matsaya kafin komawa kotun.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!