Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

Kotun shari’ar wasanni ta CAS ta kori karar Wydad Athletic

Published

on

Kotun shari’ar wasanni wato Court of Arbitration for Sport (CAS), ta yi watsi da karar da kungiyar Kwallon kafa ta Wydad Athletic Club , ta kasar Morocco ta shigar gabanta , na kalubalantar nasarar da aka baiwa Esperance a wasan karshe na gasar cin kofin nahiyar Zakarun Afirka na CAF Champions league na shekarar 2019.

A baya kungiyar ta garzaya Kotun don sake neman a dawo a buga wasan don samun Zakara bayan da hukumar CAF ta baiwa Esperance Nasara sakamakon ficewa daga filin wasa da ‘yan tawagar Wydad suka yi bayan alkalin wasa ya hana Kwallon da suka farke ta hannun Walid El Karti , ana wasan da suka nemi Alkalin wasan da ya duba na’urar Bidiyo ta VAR.

Wasan dai a ba a samu damar cigaba da buga shi ba, sakamakon kin dawowar tasu wanda hakan yasa CAF ta baiwa tawagar Esperance Nasara kasancewar ita ke jagorantar wasan da ci 2-1.

Kotun ta CAS, ta aminta da hukuncin kwamitin karbar korafi na hukumar CAF , da ya baiwa tawagar Esperance Nasara ta zama Zakaran gasar , na shekarar 2018/19.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!