Labarai
Ku mallaki makamai domin kare kanku – Sarkin Argungu

Mai Martaba Sarkin Kabin Argungu, Muhammadu Sama’ila Mera, ya bukaci al’ummar masarautarsa da su mallaki makamai bisa ka’ida domin kare kansu da yankunansu daga hare-haren ’yan bindiga da sauran masu aikata laifuka.
Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa Sarkin ya bayyana hakan ne yayin wani taro da hakimai, shugabannin ƙauyuka da na unguwanni da aka gudanar a fadarsa da ke Argungu.
Sarkin ya ce ya zama dole al’ummomi su kasance cikin shiri tare da ɗaukar matakan kariya daga hare-haren masu tayar da zaune tsaye, ya kuma ba da shawarar cewa al’umma za su iya haɗa kuɗi tare domin sayen makaman da doka ta amince da su domin kare kai.
A cewarsa, idan an mallaki irin waɗannan makamai bisa doka, ya kamata masu aikata laifuka su san cewa al’ummar yankin na da damar kare kansu, domin hakan na iya zama abin tsoratarwa da zai hana kai hare-hare.
Sarkin ya jaddada cewa addinin Musulunci ba ya ƙarfafa mutum ya zama mai rauni yayin da ake kashe jama’a, sace mutane ko cin zarafin mata.
Ya ce wajibi ne mutane su kasance cikin shirin kare rayukansu, iyalansu da al’ummominsu daga duk wata barazana.
Sai dai ya bayyana cewa ba ya ƙarfafa ɗaukar doka a hannu ko aikata tashin hankali, yana mai cewa abin da yake kira shi ne kariyar kai cikin tsarin doka, musamman ganin yadda matsalar tsaro ta yi kamari fiye da ƙarfin hukumomin tsaro kaɗai.
Sarkin ya kuma gargadi jama’a da su guji hare-haren ramuwar gayya ko kai farmaki kan wasu ƙabilu, yana mai cewa halaka marasa laifi na haifar da sabon rikici da ɗaukar fansa.
Ya ƙara da cewa duk da cewa an samu raguwar ayyukan wasu ƙungiyoyin masu tayar da hankali a yankin, har yanzu akwai wasu ’yan bindiga da ke ci gaba da addabar al’ummomi, saboda haka, ya bukaci jama’a su ci gaba da haɗa kai da hukumomin tsaro tare da kasancewa masu tsoron Allah a dukkan al’amuransu.
You must be logged in to post a comment Login