Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kudaden da aka warewa fannin noma a kasafin bana yayi kadan- Farfesa Abba

Published

on

Babban mashawarcin kungiyar gwamnoni Nijeriya a fannin noma Farfesa Abba Gambo, ya bayyana damuwa dangane da karancin kudaden da gwamnatin tarayya ta warewa ma’aikatar noma da samar da abinci a kasafin kudin bana.

Farfesa Abba Gambo ya ce kudin da aka warewa ma’aikatar na naira biliyan 110.25 bai kai ko kaso daya bisa dari na kasafin kudin bana na tiriliyan 28 ba, wadda tuni majalisun dokokin kasar suka amince da shi.

A cewar Farfesan, ‘kudaden da aka ware sun saba da yarjejeniyar da aka cimma a shekarar data gabata ta 2023 a Maputo, inda aka amince cewa kasashen Africa ciki har da Nijeriys zasu warewa fannin noma kaso goma cikin dari daga cikin kasafin kudaden su a kowacce shekara, domin samar da wadataccen abinci a nahiyar baki daya’.

 

Rahoton: Mukhtar Abdullahi Birnin

 

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!