Connect with us

Kiwon Lafiya

Kungiyar al’ummar Musulmin jihar Lagos ta bukaci Samar da kotun shari’ar mulsunci

Published

on

Kugiyar al’ummar Musulmi da ke jihar Lagos ta buka ci da a samar da kotun shari’ar musulunici da za ta dinga shari’a kan al’amuran da suka shafi addinin musulunci.

Kugiyar na mika wannan bukata ne a lokacin da suke tattaunwa da dantakar Gwamnan jihar a jam’iyyar AD mista Owolabi Salis a jiya laraba.

A cewar kugiyar al’ummar musulmi na bukatar a gina musu kotun addinin musulunci, duba da cewa a yanzu haka al’amaran musulmi na hannun wadanda ba musulmi ba ne a jihar, inda ya ce mafiya yan lokuta ba sa samun adalci.

Da ya ke maida jawabi Owolabi Salis Ya ce matukar aka zabe shi a matsayin gwamnan jihar to kuwa zai kafa kwamitin da zai duba yadda  za a samar da kotun domin amfanin al’ummar musulmin jihar.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!