Connect with us

Ƙetare

Hamas da sojojin Isra’ila sun tabbatar da kisan kwamandan rundunar sojin Hamas

Published

on

Kungiyar Hamas da sojojin Isra’ila sun tabbatar da kisan Izz al-Din Haddad, kwamandan rundunar sojin Hamas da aka fi sani da Qassam Brigades, a wasu hare-hare da Isra’ila ta kai Gaza ranar Juma’a.

Isra’ila ta bayyana shi a matsayin daya daga cikin wadanda suka kitsa hare-haren ranar 7 ga watan Oktoban 2023.

A lokacin hare-haren da aka kai da daddare an kuma kashe wasu daga cikin iyalan Haddad.

Ƙungiyoyin bayar da agaji a Gaza sun ce akalla mutum bakwai ne suka mutu a lokacin hare-haren, yayain da gommai suka jikkata.

Duk da cewa akwai yarjejeniyar dakatar da wuta tun watan Oktoban bara, gwamnatin Isra’ila na cewa tana da ikon kai hare-hare kan mambobin Hamas.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!