Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Labari mara dadi: Wadanda suka kamu da Corona sun haura 500 a Kano

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta tabbatar da cewa an samu karin mutane 65 da suka ku da cutar Covid-19 a ranar Jumu’a.

Wannan kari da aka samu ya kai jimillar masu dauke da cutar a jihar zuwa 547.

Ma’aikatar lafiya ta Kano ta wallafa a shafinta na Twitter cewa an samu karin mutum 5 da suka rigamu gidan gaskiya sanadiyyar cutar a ranar jumu’ar.

Adadin wadanda cutar ta hallaka a Kano ya kai mutum 18.

Har ila yau, a ranar an jumu’ar an sallami mutum 1 da ya warke daga cutar, wanda ya kai adadin wadanda suka warke zuwa mutum 20.

Karin Labarai:

Ma’aikatan jinya 18 sun kamu da Corona a Kano

An sallami mutum 6 da suka warke daga Corona a Kano

Yazuwa yanzu ragowar mutane 509 dake dauke da cutar na cigaba da samun kulawar jami’an lafiya a cibiyoyin killace masu dauke da cutar ta Covid-19 dake Kano.

Wannan dai na zuwa ne kwana guda bayan da aka sallami kwamishinan lafiya na jihar Kanon, cikin kunshin mutane 6 daga cikin ‘yan kwamitin yaki da cutar Covid-19 a jihar da suka kamu da cutar bayan sakamakon gwajin da akayi musu har sau biyu ya nuna cewa basa dauke da cutar a halin yanzu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!